in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin saman Najeriya ya fadi a Niamey, mutum biyu sun mutu
2013-05-07 09:46:22 cri
Mahukuntan sojin kasar Najeriya sun bayyana ranar Litini cewa, wani jirgin sojojin sama na Najeriya ya fado a Dargol kusa da Niamey, inda nan take matuka jirgin su biyu suka mutu.

Mai magana da yawun hedkwatar tsaro na kasar Burgediya janar Chris Olukolade ya bayyana cikin wata sanarwa da aka baiwa 'yan jarida a Abuja, babban birnin kasar, cewa jirgin yana aiki ne da bai shafi wani fada ba, lokacin da ya fado.

Jirgin saman na daga cikin guda hudu dake Niamey, wato cikin na aikin kafa zaman lafiya a kasar Mali da Afirka ke jagoranta.

Tuni dai an fara bincike don gano abin da ya haifar da aukuwar hadarin, in ji Olukolade tare da Karin cewa, za'a bada cikakken bayani da zaran an sanar da iyalan matuka jirgin. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China