in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin Wen Jiabao ya bukaci a mai da hankali sosai wajen magance mahaukaciyar guguwar iskar Saola da Damrey
2012-08-01 16:28:45 cri
A ranar 28 ga watan jiya, an samu mahaukaciyar guguwar iska ta Saola da Damrey a yankunan arewa maso yammacin tekun Fasific, kuma yanzu guguwar iska na dab da bakin tekun kasar Sin. Game da wannan, firaministan kasar Sin Wen Jiabao ya bayyana a yau Laraba 1 ga wata cewa, dole ne gwamnatoci a matakai daban daban su mai da hankali sosai kuma su dauki matakan rigakafi cikin tsanaki, don magance mahaukaciyar guguwar iska ta Saola da Damrey, don tabbatar da tsaron lafiyar jama'a da dukiyoyinsu.

Wen Jiabao ya ce, kamata ya yi a mai da hankali sosai game da ambaliyar ruwa da mahaukaciyar guguwa za ta kawo wa kogunan Chang Jiang da Huang He da Huai He, da kuma tabkin Tai Hu, kamata ya yi in ji Mr. Wen a hada aikin yaki da ambaliyar ruwa da magance mahaukaciyar guguwar iska tare. Ban da wannan kuma, ya zama wajibi sassan da abin ya shafa su inganta aikin sa ido game da hasashen yanayi, don shiryawa sosai wajen ceton mutane da kuma tinkarar bala'i, da mayar da aikin ceton mutane a gaban kome, kana da kara sa kulawa game da aikin yaki da ambaliyar ruwa, da kokari wajen yin rigakafin bala'in ambaliyar ruwa a duwatsu da zaizayewar kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China