in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 43 sun rasu a sanadiyyar hadarin jirgin ruwa a Gabon
2013-03-22 15:01:45 cri
Ran 21 ga wata, wani jami'in rundunar 'yan sandan sojan kasar Gabon ya bayyana cewa, ran 20 ga wata da dare, wani jirgin ruwa da ke dauke da masu sacen shiga kasar 65 ya kife a wajen tekun Esterias da ke da nisan kilomita arba'in daga arewacin babban birnin kasar, Libreville.

Jami'in ya nuna cewa, mai yiwuwa rashin kyawun yanayin a daren ne babban dalilin da ya sa jirgin ruwan ya kife, bayan tasowar iska mai karfi gami da babbar igiyar ruwa. Ya ci gaba da cewa, ya zuwa yanzu, an tsinto gawawwakin guda arba'in da uku na wadanda hadarin ya rutsa da su, amma ba a iya tabbatar da asalinsu ba.

Wani 'dan kasar Burkina Faso da ya tsira da ransa daga hadarin ya yi bayanin cewa, jirgin ruwan ya taso ne daga kasar Nijeriya kwanaki huda da suka gabata, kafin ya gamu da hadarin, kuma mafi yawan wadanda suke cikin jirgin ruwan 'yan kasashen Burkina Faso, Benin, Nijeriya da kuma wasu kasashen yammacin Afirka ne. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China