in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guguwa masu karfi sun sa an kawad da mutane dubu 549 a kasar Sin
2012-08-03 16:25:10 cri
Ma'aikatar kula da harkokin jama'a, da ofishin kula da aukuwar bala'u na kasar Sin sun kiyasta a ranar 3 ga wata cewa, guguwai masu karfin gaske masu suna 'Saola' da 'Damrey' sun riga sun sa an kawad da mutane dubu 549 a larduna 4 dake bakin tekun kasar don kaucewa gamuwa da hasara.

An ce, don tinkarar wadannan mahaukatan guguwai guda 2, a ranar 31 ga watan Yuli, ofishin kula da aukuwar bala'u na kasar Sin ya kaddamar da tsarin daukan mataki game da gargadin da aka bayar, tare da shiri sosai cikin gaggawa.

A nasu bangare, gwamnatocin lardunan da guguwan suka shafa kamarsu Jiangsu, Zhejiang, Fujian, da Shandong sun tura kungiyoyin musamman zuwa wuraren da bala'in zai fi ritsawa da su, don ba da taimako. Kana sun yi kokarin samar da kayayyakin da ake bukata kamarsu tantuna, barguna, tawulan goge jiki, don tallafa wa jama'ar da aka riga aka kawar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China