in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a nuna goyon baya ga bunkasuwar kasashe mafi koma bayan tattalin arziki
2013-10-22 17:02:14 cri

Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Wang Min ya bayyana a ran 21 ga wata cewa, tallafawa kasashe mafi koma bayan tattalin arziki da kasashe maso tasowa da ba su kusa da teku wajen samun ci gabansu na da muhimmiyar ma'ana ta fannin cimma muradun karni na MDD da bunkasuwar tattalin arzikin duniya, ya kamata, kasashen duniya cika alkawarin da suka yi na ba da taimako ga kasashen.

A gun taron da kwamiti na biyu mai kula da harkokin tattalin arziki na babban taron MDD ya kira wanda ke da jigon "kasashen dake fuskantar mawuyacin hali", Wang Min ya nuna cewa, Sin ta kan tsaya tsayin daka kan matsayin gayon bayan raya kasashen mafi koma bayan tattalin arziki da kasashe maso tasowa da ba kusa da teku ba, kuma tana kokarin taka rawarsa gwargwadon karfinta ta hanyoyi daban-daban bisa tsarin hadin kai tsakanin kasashen maso tasowa. Ban da haka, Sin ta yi alkawarin cire harajin kwastan kashi 97 bisa dari na hajjojin da take shigowa daga kasashe mafi koma bayan tattalin arziki da suka kulla dangantakar diplomasiyya tsakaninta da Sin. Sin za ta ci gaba da ba da taimakonta ga wadannan kasashe gwargwadon karfinta. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga wasu
v Saudiya ta ki karban kujeran mamban kwamitin tsaro na MDD 2013-10-18 21:05:22
v An kawo karshen shawarwari a rana ta farko kan matsalar nukiliya ta kasar Iran na sabon karo 2013-10-16 15:52:31
v Kwamitin sulhu na MDD ya la'anci hare-haren da aka kai wa sojojin kiyaye zaman lafiya a Sudan 2013-10-15 10:01:33
v Ya Kamata MDD ta jagoranci hadin kan kasa da kasa wajen yaki da ta'addanci, in ji wakilin kasar Sin 2013-10-08 16:05:49
v Sin za ta ci gaba da shiga aikin tattara kudi game da raya kasashen duniya 2013-10-08 11:11:12
v Babban sakataren MDD ya yi kira ga al'ummomin kasa da kasa da su kawo karshen tashin hankalin da ake fuskanta 2013-10-03 16:49:07
v Rukunin bincike kan makamai masu guba na MDD ya tashi daga Syria 2013-10-01 16:36:14
v An cimma matsaya guda kan hana yaduwar hamada a matakin kasa da kasa 2013-09-29 21:00:30
v Rukunin bincike na MDD kan makamai masu guba na kasar Syria ya koma kasar Syria 2013-09-25 20:28:46
v Ministan harkokin wajen kasar Sin zai halarci babbar muhawarar MDD 2013-09-22 17:10:05
v MDD ta yi Allah wadai da harin da aka kaddamar a wani babban kanti dake birnin Nairobi 2013-09-22 16:40:37
v Ana bukatar hadin gwiwwa mai karfi don cimma bukatun yaye talauci,inji rahoton MDD 2013-09-20 16:43:56
v MDD ta gudanar da bikin tunawa da ranar zaman lafiya ta kasa da kasa 2013-09-19 11:18:57
v Kwamitin sulhu na MDD ya yi tir da harin da aka kaiwa karamin ofishin jakadancin Amurka dake kasar Afghanistan 2013-09-14 17:18:12
v Kasar Sin za ta ci gaba da taka rawarta cikin MDD bisa matsayinta na wata babbar kasa mai daukar nauyin bisa wuyanta 2013-09-04 16:11:39
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China