in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira ga al'ummomin kasa da kasa da su kawo karshen tashin hankalin da ake fuskanta
2013-10-03 16:49:07 cri
A ranar Laraba 2 ga watan Oktoba ne, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga jama'a a ko ina suke a duniya da su kasance masu jajircewa wajen yin adawa da tashin hankali ta hanyar shimfida adalci, zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

A sakon da ya aike game da ranar samar da zaman lafiya, Mr. Ban ya lura da cewa, tashin hankali batu ne da ba shi da fa'ida, illa haifar da rashin adalci, nuna bambanci, da gallazawa, don haka kamata ya yi a neman mutuntawa da kare 'yancin bil-adama.

A ranar 2 ga watan Oktoban ko wace shekara ce ake yin bikin ranar yaki da tashin hankali ta kasa da kasa, don tuna ranar da aka haifi Mahatma Gandhi, jagoran kwatar 'yancin kasar India, wanda shugabannin kasashe a duniya suka yi amfani da dabaru da akidunsa na adawa da tashin hankali.

Don haka, Mr. Ban Ki-moon yake kira ga jama'a ko ina suke a wannan duniya da su yi koyi da karfin hali irin na Mahatma Gandhi, kana su yi watsi da nuna bambance-bambance da rashin nuna kauna, kana su tsaya ga nuna gaskiya da sanin ya kamata tare da rungumar hanyar sasantawa cikin lumana maimakon tashin hankali. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China