in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi zaben raba gardama cikin watan Mayu mai zuwa a kasar Ukraine, in ji jamhuriyyar Donetsk
2014-04-25 20:47:38 cri
Kwanan baya, halin da kudu maso gabashin kasar Ukraine ke ciki ya kara tsananta, a ran 22 ga wata kuwa, masu zanga-zanga dake neman shiga tarrayar Rasha sun sanar da kafa tarayyar gwamnatin wucin gadi ta jamhuriyyar jama'ar Donetsk a yayin wani taron manema labaru, tare da kuma sanar da yin zaben raba gardama a ran 11 ga watan Mayu. Ban da jihar Donetsk, ita ma jihar Luhans Ka dake gabashin kasar ta sanar da yin zaben raba gardama a wannan rana. A ran 22 ga wata, shugaban majalisar dokokin kasar Ukraine Oleksander Turchynov mai rikon mukamin shugaban kasar ya nemi sojoji da 'yan sandan kasar da su maido da ayyukan yaki da ta'addanci a gabashin kasar.

A wannan rana, Oleksander Turchynov da firaministan kasar Arseniy Yatsenyuk sun gana da mataimakin shugaban kasar Amurka Joseph Biden, bayan ganawarsu, Biden tare da Yatsenyuk sun kira taron manema labaru na hadin gwiwa, inda ya bayyana cewa, Amurka ba za ta amince da haramtaccen matakin da Rasha ta dauka na mamaye yankin Crimea har abada ba, a kokarinta, Amurka za ta ba da gudunmawa wajen dinke barakar kasar Ukraine gaba daya. Biden kuma ya kara da cewa, Amurka na ba da taimako ga Ukraine wajen warware matsalar makamashi, kuma za ta dauki matakan da suka dace don hana ko wace kasa da ta mayar da batun makamashi a matsayin makaman siyasa da za ta yi amfani da su a kan Ukraine da tarayyar Turai. Da yake tabo maganar kwaskwarima da za a yi kan siyasa da tattalin arzikin Ukraine, a cewarsa, Amurka na shirin baiwa Ukraine dalar Amurka miliyan 50 domin raya kasar daga dukkan fannoni. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China