in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi muhawara kan rahoton hakkin dan Adam na Ukraine a taron kwamitin tsaron MDD
2014-04-17 16:00:02 cri
An gudanar da taron keke da keke kan rahoton da aka gabatar dangane da yanayin hakkin dan Adam na kasar Ukraine a kwamitin tsaron MDD a ran 16 ga wata, inda wakilin kasar Rasha ya bayyana cewa, akwai rudani da rashin adalci kan wannan rahoto, a yayin da kasar Ukarine ta yi maraba da shi, kuma kasashen Amurka da Burtaniya da dai sauran kasashe sun amfani da wannan dama domin yin kira ga MDD da ta ci gaba da samar da rahotanni irin makamantan haka.

A lokacin muhawarar, mataimakin babban sakatare mai kula da harkokin kare hakkin dan Adam na MDD Ivan Simonovic ya yi bayani kan rahoton da ofishin kula da harkokin hakkin dan Adam na musamman ya fitar a ran 15 ga wata. Ya ce, hirar da ya yi tare da wakilan kananan hukumomin kasa, kungiyoyi masu zaman kansu da wasu fararen hula da dai saurasu, yayin da ya kai ziyarar aiki a kasar Crimea tun ranar 21 zuwa ta 22 ga watan Maris, kuma labaran da ya samu sun nuna cewa, an keta hakkin dan Adam a yayin kuri'ar raba gardama da aka yi a Crimea a ran 16 ga watan Maris, ciki har da sarrafa kafofin watsa labaru da dai sauransu. Bugu da kari, akwai bukatar a gudanar da bincike game da yanayin hakkin dan Adam kan ayyukan zanga-zangar da ake yi a gabashin kasar Ukraine.

Haka kuma, zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana cewa, kasar Sin na damuwa sosai game da tabarbarewar yanayin kasar Ukraine, tare da fatan bangarorin da abin ya shafa na kasar za su iya kai zuciya nesa, ta yadda za a hana kara tsanantar yanayi a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China