in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta yi kira ga Amurka da ta matsa wa Ukraine lamba
2014-04-12 16:37:44 cri
Bisa labarin da aka samu daga ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha, an ce, ministan harkokin wajen kasar Sergey Lavrov ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Amurka John Kerry a ran 11 ga wata ta wayar tarho, inda ya bukaci kasar Amurka da ta matsa wa gwamnatin kasar Ukraine lamba, don hana ta dauki matakan soja a gabashi da kuma kudancin kasar, da kuma ciyar da shawarwarin dake tsakaninta da wakilan yankin gaba, ta yadda za a iya shirya aikin gyare-gyaren tsarin mulki daga dukkan fannoni. A nasa tsokacin, Mr. Kerry ya yi alkawari cewa, kasar Amurka za ta dukufa wajen shimfida zaman lafiya a kasar Ukraine.

A wannan rana kuma, babban sakataren kungiyar tsaron arewacin tekun Atlantika ta NATO Anders Rasmussen ya bayyana cewa, kungiyar za ta karfafa aikin soja a tsakaninta da mambobi kasashen kungiyar dake makwabtaka da kasar Rasha, inda ya kuma yi kira ga mambobi kasashe da su kara kasafin kudinsu wajen aikin soja. Ya kai ziyarar aiki a kasar Bulgaria a wannan rana, inda ya jaddada bukatun karfafa hadin gwiwar mambobi kasashen kungiyar NATO kan aikin soja, da kuma kara kasafin kudi kan aikin don samun kayayyakin soja na zamani, bayan ganawarsa da shugaban kasar.

A 'yan kwanan na baya baya, ana fama da tashe-tashen hankula a yankunan dake gabashi da kuma kudancin kasar Ukraine, inda wasu yankunan kasar suke fafutukar neman 'yancin kansu domin shiga tarayyar kasar Rasha ta hanyar kuri'ar raba gardama. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China