Shugaban hukumar yanayin sama na kasar Sin Zheng Guoguang wanda ke halartar taron kwamitin zartaswa na kungiyar yanayin sama ta duniya ya bayyana a ran 16 ga wata a birnin Geneva na kasar Switzerland cewa, a cikin shekaru biyar da suka wuce, yawan asarar rayuka da tattalin arziki da kasar Sin ta samu sakamakon bala'un yanayin sama ya ragu sosai.
A wannan rana da dare, tawagar kasar Sin a wannan fanni sun yi wata liyafa tare da tawagar dindindin ta kasar Sin dake Geneva, inda a cikin jawabinsa, Zheng Guoguang ya bayyana kokari da ci gaba da Sin ta samu wajen ba da hidimma a fannin yanayin sama.
Zheng Guoguang ya ce, a shekarun baya, gwamnatin kasar Sin ta kara daukar alkawari irin na siyasa, inda ta kafa tsarin sa ido kan bala'un yanayin sama, tare da daga matsayin yin rigakafi da karfin daidaita halin ko ta kwana.
A bangare hadin gwiwa da kasashen duniya kuwa, Sin ta yi iyakacin kokari a fuskar nuna goyon bayan kan yadda za a aiwatar da tsarin ba da hidimma a fannin yanayin sama, tare kuma da ba da tabbaci ga samarwa kasashe masu tasowa dake Asiya da Afrika damar samun sukolashif guda 20 cikin dogon lokaci dangane da koyon ilmi a wannan fanni.
Babban sakataren kungiyar Michel Jarraud ya nuna godiya ga babban taimakon da Sin ta bayar a wanann fanni. Ya ce, ba za a iya tinkarar sauyin yanayi mai yanutsi a halin yanzu ba, face sai kasa da kasa sun yi hadin gwiwa a tsakaninsu. (Amina)