A wajen wani dandalin tattaunawa dangane da yadda ake kokarin raya kimiyya da al'adu a kasar Sin da aka shirya a ran nan, Mista Zheng ya bayyana cewa, ya kamata a tabbatar da zaman daidaito a tsakanin kasashe daban daban yayin da suke tinkarar matsalar sauyin yanayi, hakan ya kasance hakkin da kasashe masu tasowa suka samu bisa yarjejeniyar tsarin tinkarar matsalar sauyin yanayi ta MDD.
Sa'an nan Zheng ya kara da cewa, akwai matalauta da marasa karfi da yawa a kasar Sin, haka kuma ya kasance wuraren da ke cikin kangin talauci da yawa a kasar. Shi ya sa aikin da kasar Sin za ta yi shi ne kokarin tabbatar da samun yanayi mai kyau wajen raya kasa, haka kuma bisa matsayinta na wata babbar kasa dake dauke da nauyi a wuya, za ta yi kokarin lallashin kasashen duniya da su tinkari matsalar sauyin yanayi tare. (Bello Wang)