in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da Denis Sassou Nguesso a Congo-Brazzaville
2016-04-17 13:55:23 cri
Jiya Asabar, an rantsar da Denis Sassou Nguesso a matsayin shugaban kasar Congo-Brazzaville a birnin Brazzaville, inda shugaba Denis Sassou Nguesso, ya ce zai fara wani sabon wa'adin aikinsa na shekaru biyar ne, sannan ya bayyana cewa, cikin sabon wa'adin aikinsa mai zuwa, zai dukufa wajen cimma alkawarin da ya yi a lokacin yakin neman zaben da aka yi, domin kyautata zaman rayuwar al'ummomin kasar, da kuma ciyar da bunkasuwar tattalin arziki da masana'antun kasar gaba.

Kaza lika, ya ce, cikin shekaru biyar masu zuwa, kasar Congo Brazzaville za ta ci gaba da karfafa ayyukan samar da ababen more rayuwa, da kuma daukar matakai yadda ya kamata domin raya tattalin arzikin kasar bisa fannoni daban daban, da kyautata ayyukan kiwon lafiya a kasar, haka kuma, ya ce, za a fara ba da horo ga matasa kan wasu fasahohi domin taimaka musu wajen neman ayyukan yi, samar da karin guraben aikin yi a kasar da kuma kara karfin al'ummomin kasar wajen yin cinikayya.

Ministan harkokin gidaje da raya birane da karkara na kasar Sin Chen Zhenggao ya halarci bikin rantsuwar da aka yi a birnin Brazzaville, a matsayin manzon musamman na shugaban kasar Sin.

Haka kuma, bisa labarin da aka samu, an ce, Denis Sassou Nguesso ya lashe babban zaben ne da kashi 60.39 cikin 100 na kuri'un da aka kada a ranar 20 ga watan Maris, kuma wannan shi ne karo na biyu da ya lashe babban zaben shugaban kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China