RDC-Congo ta dauki matakan sake ingiza tattalin arziki
2016-01-28 10:59:24
cri
Gwamnatin jamhuriyar demokaradiyyar Congo ta amince da wasu matakan gaggawa guda 28 domin daidaita da sake ingiza tattalin arziki, bayan faduwar farashin albarkatun da ake hakowa. Daga cikin wadannan matakan gaggawa, musamman ma gwamnati ta dauki niyyar yaki da masu kin biya haraji da fasa kwauri a bangarorin da suka shafi tattalin arziki, sadarwa da kuma sufuri. (Maman Ada)