RDC-Congo: Tsofon faraministan Togo zai jagoranci shawarwari domin kaddamar da tattauawa
Kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta dorawa Edem Kojo, tsohon faraministan kasar Togo kana mamban kwamitin dattawa na kungiyar AU, da ya isa cikin gaggawa a birnin Kinshasa domin jagorantar shawarwarin da suka dace domin kaddamar da tattaunawar da shugaban RDC-Congo Joseph Kabila ya kira.
A cikin wata sanarwar da aka fitar a ranar Asabar, shugabar kwamitin tarayyar Afrika AU, madam Nkosazana Dlamini-Zuma, ta jaddada cewa zata cigaba da sanya ido kan shawarwarin dake gudana a RDC-Congo bisa kiran wannan zaman tattaunawa. (Maman Ada)