Manzon musamman na shugaban Sin zai halarci bikin rantsuwar kama aikin shugaban jamhuriyyar Congo
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya sanar a yau Juma'a cewa, bisa gayyatar da shugaban jamhuriyyar Congo Denis Sassou-Nguesso ya yi masa, manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping kuma ministan kula da harkokin gidaje da birane da kauyuka na kasar Sin Chen Zhenggao zai tafi birnin Brazzaville don halartar bikin rantsuwar kama aiki na shugaban kasar Sassou da za a gudanar a ranar 16 ga wannan wata. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku