in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Congo ya lashe babban zabe
2016-03-24 18:52:19 cri

Shugaba mai ci a janhuriyar Congo Denis Sassou N'Guesso, ya samu nasarar lashe zagayen farko na babban zaben kasar sa, da kaso 60.39 na jimillar kuri'un da aka kada. Ministan cikin gidan kasar Raymond Zephirin Mboulou, ya wallafa sakon dake dauke da sakamakon zaben a alhamis din nan.

A nasa bangare shugaba N'Guesso wanda ke jawabi ga mane ma labarai bayan bayyana sakamakon, ya ce hakan ya nuna burin 'yan kasar, na shiga sabuwar janhuriyar ci gaba.

Shugaba N'Guesso, mai shekaru 72 da haihuwa, zai fara sabon zangon mulki na shekaru 5 masu zuwa, biyowa bayan lashe zaben ranar Asabar din da ta gabata. Ya kuma fara mulkin janhuriyar Congo ne shekaru 32 da suka gabata.

Bisa doka kotun tsarin mulkin kasar ce ke da hurumin tabbatar da sakamakon zaben. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China