in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Congo ta sanar da kome ya daidaita bayan wata musanyar wuta a Brazzaville
2016-04-05 10:32:43 cri
Bayan kararrakin makaman yaki da aka ji a cikin daren ranar Litinin, har na tsawon sa'o'i hudu, musammun ma a cikin unguwannin kudancin birnin Brazzaville, gwamnatin kasar ta fitar da sanarwa inda ta bayyana cewa ta daidaita lamuran tare da kwantar da hankalin mazauna birnin.

A cewar hukumomin kasar, wasu mayakan sa kai na Ninja Nsiloulou suka kai ma sojojin gwamnati hari wanda ake zaton sun shigo ta kudancin Brazzaville, ta unguwar Mayanga, dake yankin na 8 na Madilou.

Sun kai hari kan sojojin gwamnati dake Mayanga, kana ofishin 'yan sandar tsakiya na Djoue, ofishin 'yan sanda na yanki na 1 na Makelekele, da kuma ofisoshin 'yan sanda na unguwannin Lemira da Kinsoundi, dukkan wadannan gine gine tare da ofshin magajin garin Makelekele, an kona su, lamarin da ke kama da wani babban aikin ta'addanci, in ji mista Thierry Moungalla kakakin gwamnatin Congo. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China