in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
RDC/Zabe: Monusco ta yi kiran da a girmama wa'adin kundin tsarin mulki
2016-04-07 10:52:58 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake jamhuriyar dimokuradiyyar Congo (Monusco) ta bayyana a ranar Laraba cewa shirin zabe da ke gudana yanzu dole ne yayi la'akari da wa'adin kundin tsarin mulki.

A bangaren MDD, karara ne cewa muna fatan shirin zabe yayi la'akari da wa'adin kundin tsarin mulki, in ji Charles Antoine Bambara, darektan watsa labarai na Monusco.

A ganin mista Bambara, akwai bukata na gudanar da tattaunawa da za ta iya bada damar cimma wani jadawali da za a yi amfani da shi a ranaku masu zuwa.

Ina ganin wannan yana da muhimmaci sosai. Kuma yanzu, gaskiya ce cewa idan aka fara shirya wannan tattaunawa, dole ne dukkan masu ruwa da tsaki na siyasar RD-Congo su amince cimma wata yarjejeniya. Ta wannan ne idan suka cimma yarjejeniya za a iya ganin idan, mu a bangaren gamayyar kasa da kasa, mu ga wani jadawalin aiki ya fito daga wadannan shawarwarin tattaunawa, za'a a ganin wace irin shawara ce MDD za ta dauka a wannan lokaci, in ji mista Bambara. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China