in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar jam'iyyar adawa a Congo ta yi kiran kasashen duniya da su yaki da ta'addanci
2016-01-31 13:07:15 cri
Babban sakataren jam'iyyar hadin kan Afrika domin tabbatar da demokuradiyar jama'a (UPADS, kuma babbar jam'iyyar adawa a Congo), Pascal Tsaty-Mabiala, ya yi kira a ranar Asabar a birnin Brazaville ga kasashen duniya da su kebe duk wasu dabarun da suka dace domin yaki da barazanar ta'addanci.

Barazana ga zaman lafiya a cikin kasashen duniya ita ce ta'addanci. Duk wasu matakan tsaro da duk wasu dabarun yaki ya kamata a tanade su, in ji mista Tsaty-Mabiala a yayin bikin bude zaman taron musammun na kwamitin kasa na jam'iyyar UPADS.

Babbar matsalar, ita ce barazanar ta'addanci dake bazuwa a yankin Sahel a halin yanzu tare da tsirarrun kungiyoyin ta'addanci kamar AQMI da Ansar-Dine da sauransu.

A cewar mista Tsaty-Mabiala, kasar Congo, dake iyaka da Kamaru da Afrika ta Tsakiya, ba za ta tsira ba har nan zuwa wani lokaci kuma dole ta nuna damuwa.

Kusa da kan iyakokin wasu kasashen Afirka, kungiyar Boko Haram na gudanar da ayyukan ta'addanci a kasashen Najeriya, Chadi, Nijar da Kamaru, tare da nuna cewa ci gaban da kungiyar IS take samu na kokarin kafa daular kasar musulunci na zama bazarana ga zaman lafiya a duniya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China