in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birtaniya za ta ji ra'ayin jama'arta kan dangantakar dake tsakaninta da EU
2016-02-21 13:24:39 cri
Firaministan kasar Birtaniya Mista David William Donald Cameron ya sanar a jiya cewa, Birtaniya za ta kada kuri'ar jin ra'ayin jama'a a ranar 23 ga watan Yunin bana don yanke shawarar, ko Birtaniya za ta ci gaba da zama a cikin EU ko a'a..

Mista Cameron ya bayyana hakan ne bayan kammala taron majalisar ministocin kasar a wannan rana, ya kuma shedawa manema labaru cewa, gwamnati za ta shirya yadda jama'arta za su yarda da ci gaba da kasancewar Burtaniya cikin EU, a cewarsa, matakin da zai taimakawa Birtaniya wajen samun karin zaman lafiya, karfi da wadata saboda ganin kwaskwarima da EU ta yi, idan ba haka ba, barin EU zai jefa Birtaniya cikin mawuyacin hali na koma bayan tattalin arziki da rashin tsaro.

A gobe ne ake saran Mista Cameron zai gabatar da jawabi a majalisar dokokin kasar don kaddamar da shirin kuri'ar jin ra'ayin jama'ar.

Bayan da aka shafe kwanaki biyu ana kokarin cimma matsaya a taron kolin na EU, a karshe Mista Cameron da sauran shugabannin EU sun kai ga cimma matsaya daya don biyan wasu bukatun Birtaniya, ciki hadda rage tallafin da ake baiwa 'yan cin rani a Birtaniya, rashin shiga shirin karin dunkulewar Turai, da kuma matakan da suka shafi ba da kariya ga kasashen da ba sa amfani da kudin Euro da sauransu. Duk da hakan, 'yan kasar Birtaniya na bayyana fatansu matuka na ganin kasar ta janye daga EU. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China