in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ceto mutane 126 a Burkina Faso
2016-01-16 18:06:03 cri
Jami'in hukumar tsaro ta kasar Burkina Faso ya bayyana a yau Asabar 16 ga wata cewa, an gama ceto mutane da aka yi garkuwa da su cikin harin da aka kai a wani Otel din Splendid dake birnin Ouagadogou na kasar Burkina Faso, inda aka ceto mutane 126 sannan aka harbe 'yan ta'adda 3.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, an kuma kai hari kan wani Otel na daban dake dab da Otel din Splendid, kuma rundunar tsaron kasar suna kan hanyar zuwa wannan wuri. Ban da wannan kuma, manyan asibitocin kasar dake birnin Ouagadougo hedkwatar kasar na baiwa mutane fiye da 40 jiyya.

Idan ba a manta ba, a daren jiya Juma'a 15 ga wata, wassu 'yan ta'adda sun mamaye wannan Otel tare da yin garkuwa da mutane da dama, ba da dadewa ba rundunar tsaro sun isa wuri tare da kewaye Otel da tankoki da motocin yaki, kuma sun yi musayar wuta da masu fafutuka. An ce, rundunonin soja na musamman na kasashen Faransa da Amurka sun shiga aikin ceto. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China