in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan majalisa 14 da suka fito daga jam'iyyun siyasa 7 sun kafa wani gungu a majisalar dokokin Burkina Faso
2015-12-29 10:08:53 cri
'Yan majalisa goma sha hudu da suka fito daga wasu jam'iyyun siyasa bakwai na kasar Burkina Faso, sun kafa a ranar Litinin a birnin Ouagadougou, wani gungun 'yan majalisa domin nuna goyon baya ga zababben shugaban kasar, mista Roch Marc Christian Kabore.

Wadannan jam'iyyun siyasa daga cikinsu akwai kawancen jam'iyyar UNIR/PS na mista Benewende Sankara, wani babban mai adawa da tsohon shugaban kasa Blaise Compaore a tsawon tarihi. An kafa wannan gungun 'yan majalisa dake kuma cikin kawancen jam'iyyu maso rinjaye dake goyon bayan shugaban kasa domin kare maradun kasar da kuma amsa bukatun al'ummar kasar a bangarori daban daban, cewar kakakinsa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China