in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari kan sansanin AU dake Somaliya
2016-01-15 19:34:36 cri
An kai hari a wani sansanin soja na kungiyar tarayyar kasashen Afrika AU dake Somaliya a Juma'an 15 ga wata, sai dai ba a kai ga sanin hakikanin yawan mutanen da aka yi asara ba.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, wani kakakin kungiyar Al shabaab ya ce, kungiyar ta dauki alhakin kai wannan harin a wannan sansanin dake kan iyakar da ke tsakanin Somaliya da Kenya, wadda ke kunshe da sojojin daga kasar Kenya.

An ba da labarin cewa, sojojin sansanin suna ci gaba da yin musayar wuta da 'yan kungiyar, abinda yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China