in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 133 sun mutu sakamakon zazzabin Dangue
2015-12-25 12:30:30 cri

Hukumar kiwon lafiya ta kasar Sudan ta bayyana cewa, sakamakon barkewar cutar zazzabin Dangue a karshen wata Agustar da ya shude a yankin Darfur na kasar, an samu kimanin mutane 571 wadanda cutar ta kama, inda cikinsu 133 sun rasa rayukansu.

Hukumar ta kuma ce bisa kididdiga, kimanin kashi 91.5 bisa dari cikin wadannan mutane su 571 da suka kamu da cutar, suna zaune ne a yankin Darfur, kuma adadinsu ya kai mutum 523, daga cikinsu 128 sun rasa rayukansu. Ban da wannan kuma, a cikin larduna 5 na kasar, jihar yammacin Darfur, da arewacin Darfur, na kan gaba wajen yawan masu kamuwa da cutar, inda yawansu ya kai kimani kashi 80 cikin dari.

Ya zuwa yanzu, hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, ta tura masananta masu aikin jiyya zuwa wadannan wurare, domin jagorantar aikin dakile yaduwar wannan cuta da kuma aikin rigakafi, kana za su gudanar da hadin gwiwa da masu aikin jiyya na kasar Sudan don bada taimako yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China