in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari ga ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD a yankin Darfur
2013-08-13 21:15:35 cri
Mataimakin kakakin babban sakataren MDD Eduardo del Buey ya bayyana a ranar 12 ga wata cewa, an kai hari ga wani rukunin suntiri na tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD da kungiyar AU wato UNAMID a yankin Darfur dake kasar Sudan, wanda ya haddasa raunatar ma'aikacin tawagar daya.

Eduardo del Buey ya ce, bayan da aka kai hari ga wannan rukuni a yankin Adila, sojojin kiyaye zaman lafiya sun tura wani rukunin soja zuwa yankin don bada taimako. Ya zuwa yanzu, babu wani karin haske dangane da wannan hari.

Eduardo del Buey ya kara da cewa, tawagar UNAMID ta riga ta samu wani rahoto game da hali mai tsanani da ake ciki a yankin Adila a ranar 10 ga wata. Bayan haka ne, a ranar 12 ga wata, tawagar ta UNAMID ta samar wa hukumar yankin Darfur jirgin sama da zai tafi zuwa yankin Adila tare da sauran abubuwan taimako don taimakawa hukumar wajen kawo karshen rikicin da ake fama da shi a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China