in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya yi Allah wadai da kisan ma'aikatan lafiya a Yammacin Dafur
2013-11-30 17:05:03 cri
Babban jami'in ofishin MDD mai lura da ayyukan jin kai a kasar Sudan Ali Al-Za'tari, ya yi tir da kisan wasu ma'aikatan hukumar kula da lafiya ta kasar su 2, wadanda ke cikin tawagar masu ba da allurar rigakafin cutar kyanda a Yammacin Dafur.

An ce, wasu mahara ne da ba a san ko su waye ba, suka hallaka jami'in lafiyar guda da direbansa a ranar Litinin din da ta gabata, yayin da suke tsaka da gudanar da aikin na rigakafi, wanda aka fara tun ranar 24 ga watan Nuwambar da ya shude.

Da yake karin haske kan dalilan aiwatar da rigakafin, Al-Za'tari, ta bakin kakakin MDD Martin Nesirky, ya ce, Asusun UNICEF, da hadin gwiwar hukumar lafiya ta WHO ne ke daukar nauyin wannan aiki, da nufin kare yara kanana kimanin miliyan 15 dake kasar daga kamuwa da wannan cuta ta kyanda.

Daga nan sai ya yi kira da dukkanin masu ruwa da tsaki, da su tabbatar da kare rayukan ma'aikatan da ke gudanar da wannan aiki a dukkanin sassan kasar ta Sudan, tare da tabbatar da dukkanin yaran kasar sun karbi wannan allura ta rigakafi. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China