in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar Dinkin Duniya ta ce yakin da ake yi a kudancin Sudan, ya sanya jama'a fiye da dubu 15 rasa muhallan su
2014-03-05 17:33:41 cri
Wasu jami'an Majalisar dinkin duniya, sun bayyana cewar, yakin da ake yi na baya-bayan nan a Darfur dake kudancin Sudan ya haddasa samar da yan gudun hijira fiye da dubu 15.

Jami'an majalisar dinkin duniyar a Sudan, sun ce mafi yawa daga cikin wadanda suka arcewa batakashin, sun garzaya ne zuwa sansanonin 'yan gudun hijira na Al-Salam da Kalma wadande ke wajen Nyala babban birnin jihar South Darfur.

Mukaddashin shugaban gudanarwa na majalisar ta dinkin duniya a Sudan, Adnan Khan, ya nuna matukar damuwa a game da rahotannin dake nuni da cewa dubannnin jama'a sun gudu daga gidajen su, a sakamakon barkewar gumuzu tsakanin kungiyoyi masu dauke da makamai da kuma sojojin Sudan, gami da kananan kungiyoyin dakarun soji dake yankin Um Gunya a Kudancin Darfur. (Suwaiba Sule)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China