in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani harin da aka kai ya halaka ma'aikatan kiyaye zaman lafiya a Darfur
2014-10-17 10:38:42 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana a ranar 16 ga wata cewa, an kai hari ga tawagar musamman ta MDD da kungiyar AU dake yankin Darfur a jihar arewacin Darfur dake kasar Sudan, wanda ya haddasa mutuwar ma'ikatan kiyaye zaman lafiya 3.

Ban Ki-moon ya bayar da sanarwa ta hannun kakakinsa, inda ya yi tir da wannan hari. Sanarwar ta ce, an kai hari ga ma'aikatan kiyaye zaman lafiya da suke bada kariya ga wani tabki dake dab da birnin Korma na jihar arewacin Darfur, wanda ya haddasa mutuwar ma'aikatan kiyaye zaman lafiya 'yan kasar Habasha 3. Ban Ki-moon ya jaddada cewa, ba za a amince da kai hari kan ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD ba, wanda hakan ya saba wa dokokin duniya.

A wannan wata, an sha kai hare-hare kan ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD a yankin Darfur na kasar Sudan, kasar Mali, da kasar Afirka ta Tsakiya da sauran wurare, wadanda suka haddasa mutuwar ma'aikatan kiyaye zaman lafiya fiye da 10. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China