in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD a bincikenta na farko ba ta gano shaidan cin zarafin mata da aka yi zargi a Darfur ba
2014-11-11 17:04:26 cri
Kwamitin AU da MDD da ke aiki a Darfur na kasar Sudan ya bada rahoton cewar bincikensa a farko bai gano zargin da aka yin a cin zarafin mata da aka yi a birnin Tabit ba, kamar yadda kakakin majalissar ya bayyana ma manema labarai ranar litinin din nan.

Frahan Haq ya ce bayan samun dama a ranar lahadi don a gudanar da bincike a kan zargin cin zarafin mata da 'yan mata fiye da 200 na yi masu fyade a garin dake arewacin Darfur, kwamitin na AU da MDD dake aiki a yankin UNAMID yace tun safiyar wannan rana yayi ta zagayen kauye yana tambayar mazauna da su bada bayanin iya abinda suka sani game da labarin da kafofin yada labarai suka watsa.

Kungiyar masu binciken da suka hada da wakilan 'yan sanda, sojoji da fararen hula har ila yau sun gudanar da tambayoyin ga kwamandar sojojin kasar ta Sudan, wanda a cewar Mr. Haq babu wanda ya tabbatar da faruwan haka a wannan garin na Tabit a ranar da kafofin watsa labarai suka yi ta yadawa.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China