in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi tir da kisan jami'in wanzar da zaman lafiya a Arewacin Darfur
2014-05-25 15:52:59 cri
Kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da wani hari da aka kai, kan tawagar ma'aikatan wanzar da zaman lafiya ta MDD a Arewacin Darfur, a Asabar 24 ga wata, harin da ya yi sanadiyar hallaka jami'i daya tare da jikkata wasu jami'an su 3.

Mambobin majalissar dai sun bayyana takaicin nasu ne a jiya Asabar, suna masu kira da a tabbatar da hukunta wadanda suka aikata wannan ta'asa.

Rahotanni sun ce jami'in da ya rasa ransa yayin harin na ranar Asabar dan asalin kasar Rwanda ne, ya na kuma tare da sauran wadanda suka samu raunuka, cikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta UNAMID, wadda ke aikin sulhunta wasu kabilun yankin Arewacin Darfur a garin Kabkabiya, lokacin da aka kai musu harin. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China