in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin yada labaru ya gudanar da taron manema labaru bayan an kammala taron sauyin yanayi
2015-12-24 14:23:38 cri
A jiya ne ofishin yada labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da wani taron manema labaru na gida da na waje, inda wakilin musamman na kasar Sin a taron sauyin yanayi na birnin Paris Xie Zhenhua, da kuma shugaban sashin kula da tinkarar sauyin yanayi na kwamitin raya kasa da yin kwaskwarima na kasar Sin da sauran jami'ai suka yi bayyani kan rawar da Sin ta taka a taron sauyin yanayi da kuma matakan da Sin take dauka na rage fitar da gurbatacciyar iska da yin tsimin makamashi.

Mista Xie ya yi bayyani cewa, an kammala taron sauyin yanayi na birnin Paris na tsawon kwanaki 13, taron da ya gudana daga ran 30 ga watan Nuwamba zuwa ran 13 ga wannan wata. Shugaban kasar Sin Xi jinping ya halarci bikin bude taro tare da ba da jawabi mai muhimmanci. Daga karshe an kai ga cimma yarjejeniyar Paris dake shafar bangarori daban-daban cikin adalci bayan kokarin da kasa da kasa suka yi, ita ma tawagar Sin ta taka rawa mai yakini a taron.

Ban da wannan kuma, Mista Xie ya kara da cewa, yarjejeniyar ta nemi dukkannin kasashe da su dauki mataki bisa halin da suke ciki, tare da la'akari da irin bambancin dake tsakaninsu gwargwadon karfinsu, ko da yake a cewarsa, akwai wasu matsala a cikin yarjejeniyar, misali batun kudi da musayar fasahohi. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China