in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya bukaci da a yi koyi da Sin a fannin tunkarar kalubalen sauyin yanayi
2015-12-08 10:11:04 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya ja hankalin kasashe mambobin MDD da su yi koyi da irin matakan da kasar Sin ke dauka game da tunkarar kalubalen sauyin yanayi cikin hadin gwiwa.

Mr. Ban ya bayyana hakan ne ga mahalarta taron sauyin yanayi na birnin Faris. Ya ce, sanarwar hadin gwiwar Sin da Amurka game da sauyin yanayin, wadda ta kunshi manufofin kasashen biyu na shawo kan matsalar nan da shekaru 15 masu zuwa, wani babban ginshiki ne na cimma nasarar da ake fata.

Kaza lika ita ma sanarwar hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da Faransa game da sauyin yanayin, wadda aka sanyawa hannu yayin ziyarar da shugaban kasar Faransa ya kai kasar ta Sin a farkon watan Nuwamba, a cewar Mr. Ban, mataki ne da ya cancanci matukar yabo.

Babban magatakardar MDDr ya kara da cewa, bayan warware manyan sassan da ake da sabani a kan su game da matsalar sauyin yanayi, abu na gaba shi ne koyi daga irin yarjejeniyoyin da Sin ta kulla tsakanin ta da Faransa da kuma Amurka, bisa matsayi da kowa zai aminta da shi.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China