in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin ya yi jawabi game da sakamakon taron tinkarar sauyin yanayi na Paris
2015-12-13 17:30:23 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana a ranar 13 ga wata cewa, jiya an cimma yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi ta Paris da sauran sakamako a yayin wannan taron Paris, wanda yake da babbar ma'ana wajen kokarin tinkarar sauyin yanayi, kuma kasar Sin ta nuna maraba da sakamakon da aka cimma game da wannan batu.

Hong Lei ya bayyana cewa, Sin tana sa kaimi ga cimma nasara a shawarwarin Paris. Har ma sau da yawa ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayar da sanarwoyin hadin kai tare da sauran shugabannin kasashen duniya game da wannan batu, baya ga yadda ya halarci bikin bude taron na Paris, tare da gabatar da wani muhimmin jawabi kan yadda za a inganta hadin gwiwa domin tinkarar sauyin yanayi, wanda ya kasance wata muhimmiyar shawara a siyasance game da batun. Tawagar kasar Sin ta shiga shawarwarin cikin yakini bisa ra'ayin daukar nauyin dake bisa wuyanta da hadin gwiwa, wadda ta samar da gagarumar gudummawa wajen cimma yarjejeniyar Paris. Hakan ya sheda cewa, Sin ta dauki alhakinta a matsayinta ta wata kasa mai girma dake nuna kwazonta wajen tinkarar sauyin yanayi.

Hong Lei ya kara da cewa, taron Paris wani sabon mafari ne na hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa wajen tinkarar sauyin yanayi. Kasar Sin za ta yi kokari tare da kasa da kasa wajen ci gaba da samar da gudummawa kan tinkarar sauyin yanayi a duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China