in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na shugaban kasar Sin ya gana da sabon shugaban kasar Tanzaniya
2015-11-07 13:50:50 cri
Manzon musamman na shugaban kasar Sin kuma mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Mista Zhang Ping ya gana da John Magufuli bayan bikin rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasar Tanzaniya.

Mista Zhang a lokacin ganawar ya isar da kyakkyawar fata daga shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa sabon shugaba John Magufuli, inda ya ce Sin na dora babban muhimmanci kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Haka kuma Sin tana fatan zurfafa hadin gwiwa da Tanzaniya a dukkanin fannoni da kuma kawo moriyar juna da samun bunkasuwa tare, sannan kuma Sin na gayyatar Shugaba John Magufuli da ya halarci taron koli na dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afrika da za a kira a farkon watan Disamba a birnin Johannersburg na kasar Afrika ta Kudu.

A nasa bangare kuwa, Mista John Magufuli ya nuna godiya ga zuwan Mista Zhang a bikin rantsar da shi, kuma ya isar da gaisuwarsa ga shugaba Xi Jinping ta bakin Mista Zhang, inda ya yi fatan dukufa kan raya dangantaka tsakanin kasashen biyu a wa'adinsa. Mr. Magafuli har ila yau ya bayyana fatan kara yin hadin gwiwa da Sin don kai dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi. Ban da wannan kuma, Mista John Magufuli yana nuna kyakkyawar fata na samun ci gaba mai armashi a taron koli da za a yi a Afrika ta Kudu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China