in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rushewar wani gini ya haddasa mutuwar mutane 36 a Tanzaniya
2013-04-02 16:24:47 cri
A ranar 1 ga watan Afrilu, an kammala aikin ceton mutanen da wani gini a birnin Dar es Salaam wato birni mafi girma da ke kasar Tanzaniya ya fadawa. Haka nan, an gama aikin shara a wurin da ginin ya fadi, tuni kuma, rundunar 'yan sanda ta sanar da cewa, mutane 36 sun rasu sakamakon aukuwar lamarin.

A wajen hadarin, direktan hukumar 'yan sandan yankin Dar es Salaam Suleiman Kova, ya sanar da cewa, mutane 36 sun mutu cikin wannan hadari, cikinsu har da wasu kananan yara. Kova ya ce, yanzu rundunar 'yan sanda ta fara tuhumar shugaban kamfanin gine-ginen ginin, da babban injiniya, da mai tantance ingancin ginin, da wasu mutane 6, inda bayan an tabbatar da kwarya-kwaryar sakamakon binciken, za a gabatar da wadanda ake zargi gaban kuliya.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China