A wannan rana, shugaban hukumar zabe ta Zanzibar Jecha Salum Jecha ta gidan rediyon Zanzibar ya sanar da cewa, sakamakon tabka magudi cikin zaben shugaban kasa da zaben majalisar dokoki, wato an keta dokar zabe da tsarin mulkin Zanzibar, shi ya sa aka soke sakamakon zaben, don haka za a sake shirya wani zaben. Ya kuma bukaci jama'a da su kai zuciya nesa, su jira karin bayani na nan gaba, amma bai bayyana lokacin da za a sake gudanar da zaben ba.
A wannan rana, hukumar zabe ta Tanzaniya ta bayyana cewa, soke sakamakon zabe a Zanzibar ba zai kawo tasiri game da babban zaben kasar Tanzaniya ba.(Bako)