Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Madam Hua Chunying, ta bayyana cewa, mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Mista Zhang Ping, a matsayin manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, wanda zai halarci bikin rantsar da sabon zababben shugaban kasar Tanzaniya John Magufuli.
Mr. Zhang zai wakilci shugaba Xi ne a wajen bikin rantsuwar, bisa gayyatar shugaban kasar ta Tanzania mai ci Jakaya Kikwete, bikin da ake fatan gudanar gobe Alhamis a birnin Dares Salaam. (Amina Xu)