in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Tanzaniya ya gana da manzon musamman na Mista Xi Jinping
2014-04-28 14:50:38 cri

Shugaban kasar Tanzaniya Jakaya Kikwete ya gana da manzon musamman na shugaban kasar Sin Mista Xi Jinping, kuma mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Mista Chen Changzhi.

Bayan Mista Chen ya isar da sakon Xi Jinping na taya murnar cikon shekaru 50 na kafuwar Jamhuriyar Tarayyar Tanzaniya. Kafin ya bayyana cewa, Sin tana son yin kokari tare da Tanzaniya, domin zurfafa hadin kai da abokantaka a fannoni daban daban a tsakaninsu.

Kikwete ya nuna godiya ga takwaransa na Sin Xi Jinping da ya turo manzon musamman Chen ya halarci bikin taya murnar cikon shekaru 50 na kafuwar kasar a madadinsa. Ya ce, kasar Sin babbar abokiyar Tanzaniya ce, inda kana Tanzaniya na daukar kasar Sin a matsayin wata muhimmiyar abokiyartar hadin gwiwa. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China