in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin raya Afrika na fatan hadin gwiwa da kasar Sin don cimma mafarkin Afrika
2015-10-22 19:31:40 cri
Mataimakin shugaban bankin raya Afrika(ADB) Mista Rémy Rioux ya bayyana a yau Alhamis cewa, yanzu ana samun muhimman canje-canje a Afrika, don haka akwai bukatar taimako da hadin gwiwa da kasar Sin a fannin hada-hadar kudi da zuba jari, ta yadda nahiyar za ta cimma burinta.

Mista Rémy Rioux wanda ya bayyana hakan a taron dandalin kasashen da kasuwanninsu ke tasowa na shekarar 2015 da aka yi a birnin Beijing cewa, ko da yake Afrika na samun ci gaba a 'yan shekarun baya, har yanzu nahiyar tana fuskantar kalubaloli daban-daban, ciki hadda matsalar bunkasuwar tattalin arziki, karancin muhimman ababen more rayuwa, rashin isassun guraben aikin yi da sauransu. Don haka ya ce, ya kamata Afrika ta kara zuba jari a bangaren muhimman ababen more rayuwa, ko da yake ana fama da karacin kudade a wadannan fannoni. Ban da wannan kuma, bukatar da Afrika ke da ita a fannin zirga-zirga, makamashi, sadarwa da sauransu ta kara samar da zarafi mai kyau ga kasuwanni masu tasowa ciki hadda kasar Sin. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China