in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fitar da bayani game da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afrika a shekarar 2013
2013-08-29 10:59:53 cri
Ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwa ta kasar Sin a yau Alhamis 29 ga wata ya fitar da bayani mai taken "hadin gwiwa dake tsakanin kasar Sin da Afrika ta fuskar tattalin arziki da cinikayya a shekarar 2013", inda aka bayyana sabon ci gaba da bangarorin biyu suka samu a fannin hadin kai kan tattalin arziki da cinikayya a dukkan fannoni a 'yan shekarun baya.

A shekarar 2010 ne ofishin ya fitar da irin wannan takardar bayani a karo na farko. Takardar bayanin na wannan karo ya nuna yadda kasar Sin da kasashen Afrika suka inganta hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da cinikayya, tare kuma da neman hanyar samun bunkasuwa tare, ciki har da inganta samun dauwamammen ci gaban cinikayya, karfafa harkokin zuba jari da tattara kudi, karfafa hadin gwiwa kan aikin gona da samar da isassun hatsi, bada tallafi ga kasashen Afrika don samar da muhimman kayayyakin more rayuwa, mayar da hankali kan neman ci gaban kasashen Afrika ta fuskokin zaman rayuwar jama'a da kara karfinsu, da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin bangarori da dama. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China