in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan taimakawa kasashen Afrika wajen kawar da talauci
2013-07-10 16:43:28 cri
Mataimakin direktan cibiyar saukaka fatara ta kasar Sin Huang Chengwei ya bayyana a gun wani taro karo na hudu talauci tsakanin Sin da Afrika dangane da rage da aka yi a ran 9 ga wata a birnin Hangzhou na kasar Sin cewa, hadin kan Sin da Afrika wajen rage talauci ya kasance wani muhimmin dandali game da raya dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu. Sin na fatan kara yin mu'ammala tsakanin bangarorin biyu a fannin rage talauci ta yadda za a yi musayar ilmi da fasahohi ta wannan fanni.

Huang Chengwei ya ce, hadin gwiwa dake tsakanin Sin da Afrika ba ma kawai yana da muhimmanci ga sha'anin rage talauci a duniya ba, har ma zai taimaka wajen samar da jituwa a kasar Sin da Afrika. Sin na fatan nuna wa kasashen Afirka irin basira da ilmin da ta samu cikin shekaru 30 da suka gabata, ta yadda kasashen Afrika cimma nasarar rage talauci bisa yanayin da suke ciki.

Wakilin hukumar shirin raya kasashe na MDD wato UNDP dake kasar Sin Patrick Haverman ya ce, UNDP yana ta hadin gwiwa da kasar Sin a fannin sa kaimi ga hadin kai tsakanin kasashe masu tasowa. Ya yi alkawarin ci gaba da nuna goyon baya ga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afrika, tare kuma da ba da gundumawa wajen tabbatar da dauwamammen ci gaba a shiyya-shiyya da ma duniya baki daya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China