in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan ba da gudunmawa wajen gina manyan ababen more rayuwa a Afrika
2014-05-13 20:35:00 cri
Kasar Sin na fatan kara hadin kai da kasashen Afrika ta fuskar musanyar ra'ayi kan shimfida hanyoyin jiragen kasa da fassahohi da dabaru, ta yadda za ta ba da gudunmawa wajen gina manyan ababen more rayuwa a Afrika, har ma da kara tuntubar juna tsakanin Sin da Afrika.

Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Hua Chunying wadda ta bayyana hakan ta ce a lokacin ziyarar firaministan kasar Sin Li Keqiang a Afrika,ya gana da shugabannin kasashen Kenya, Uganda, Tanzaniya, Ruwanda, Sudan da Burundi da sauransu kan yadda za a raya gabashin Afrika.

Ta yi bayanin cewa bayan ganawar Shugabannin sun cimma matsaya daya kan kafa wata hanyar jirgin kasa dake hada wadannan kasashen da kuma kafa yankin raya tattalin arzikin bai daya a tsakaninsu.

Game da wannan batu, Madam Hua tayi bayani ma manema labarai a safiyar talatan nan 13 ga wata a nan birnin Beijing cewa, Mr Li Keqiang ya cimma nasarar ziyarar kasashen hudu na Afrika kuma a lokacin ziyarar tasa ya halarci bikin sa hannu kan yarjejeniyar shimfida hanyar jiragen kasa tsakanin Mombasa da Nairobi na kasar Kenya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China