in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron tattaunawa game da sha'anin al'adu tsakanin Sin da Afrika a nan birnin Beijing
2013-06-19 16:10:11 cri
An bude taron tattaunawa game da sha'anin al'adu tsakanin Sin da Afrika a ran 19 ga wata a nan birnin Beijing fadar gwamnatin kasar Sin, wanda ya kasance muhimmin taro cikin ayyukan yada al'adun kasar Sin na shekarar 2013. Taron wanda hukumar al'adu ta kasar Sin ta shirya ya samu mahalarta kimanin 120 ciki hadda jami'an kasar Sin da jami'an hukumomin al'adu na kasashen Afrika 26, jami'in kungiyar AU mai kula da harkokin al'adu, masana da kwararu.

Mataimakin ministan al'adun kasar Sin Zhao Shaohua ya bayyana cewa, hadin gwiwa da Sin da Afrika ke yi a dukkan fannoni ciki hadda fannin al'adu ya dace da halin da ake ciki, a matsayin wani sabon sha'anin raya tattalin arziki da al'ummar bangarorin biyu, ba ma kawai al'adu ya kasance muhimmin jigo a shirin hadin gwiwa tsakaninsu ba, har ma yana da alaka da habaka hadin kai a fannin tattalin arziki da ciniki, sannan zai yi amfani sosai wajen gaggauta sabuwar dangantakar hadin kai bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni cikin dogon loakci tsakaninsu.

A lokacin wannan taro da za'a rufe a ran 24 ga wata, mahalartan zasu tattauna kan wasu manyan batutuwa ciki hadda halin da ake ciki na raya sha'anin al'adu, fasahohi da aka samun, burin yin hadin kai da sauransu. Ban da haka, za a kafa wani dandalin tuntubar juna tsakanin Sin da Afrika kan sha'anin al'adu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China