in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yukurin hadin kai da kasashen Afrika amma ba bisa burin raya nahiyar ba,kuskure ne
2014-01-08 20:58:02 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Madam Hua Chunying ta bayyana cewa, kuskure ne idan an yi yunkurin hadin kai da kasashen Afrika amma ba da burin raya nahiyar ba, kuma ba za a cimma nasara ba ko kadan,don haka kasar Sin na fatan ganin kasashen duniya su dauki matakan da suka dace wajen yin hadin kai da kasashen Afrika.

A gun taron manema labaru da aka yi a laraban nan 8 ga wata a nan birnin Beijing fadar mulkin kasar Sin, Madam Hua ta yi bayani dangane da tambayar da aka yi mata cewa ko ziyarar da ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi ya yi a wasu kasashen Afirka a wannan karo, mataki ne da Sin ta dauka domin takara da Japan, inda Madam Hua ta ce, ziyarar ministan a nahiyar Afrika a farkon ko wace shekara, shiri ne da shugabannin kasar Sin suka dade suna yi, abin da ke nuna cewa, Sin ta dora muhimmanci sosai kan zumunci dake tsakanin bangarorin biyu. Tana mai cewa, manufar Sin a bayyane take, kuma tana kokarin sa kaimi ga kasashen duniya da su yi hadin kai da nahiyar Afrika, domin taimaka wa wajen wanzar da zaman lafiya, tabbatar da tsaro da raya Afrika. Bugu da kari, Sin na fatan kasa da kasa su daidaita tunaninsu kan aikin hadin kai da za su yi tsakaninsu da kasashen Afrika, saboda a cewar ta ya kamata su mai da hankali kan kawo amfani ga jama'ar kasashen Afrika, kada su samu kuskure a ciki. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China