in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da bikin gabatar da alamar Afrika ta kudu a nan birnin Beijing
2014-12-22 21:31:27 cri
Jaridar China Daily da hukumar Brand South Afrika cikin hadin gwiwwa sun kaddamar da wani biki na gabatar da alamar kasar Afrika ta kudu a yau Litinin 22 ga wata a nan birnin Beijing. A lokacin wannan biki, Babban jakada mai kula da harkokin cinikayya na Afrika ta kudu Greg Munyai ya bayyana fatan sa na ganin an zurfafa zumunci tsakanin kasashen biyu ta yin amfani da kafofin yada labaru, tare kuma da daga matsayin juna cikin jama'ar kasashen biyu.

Saboda ganin wannan shekarar da muke ciki, shekarar Afrika ta kudu ne ga kasar Sin, hukumomin daban-daban na Afirka ta kudu sun gudanar da ayyuka masu yawa domin gabatar da alamar Afrika ta kudu a nan kasar Sin karkashin jagorancin ofishin jakadancin Afrika ta kudu. Greg Munyai ya ce, za a gudanar da shekarar Sin a Afrika ta kudu a shekara mai zuwa, gwamnatin kasar Afrika ta kudu na fatan karban karin Sinawa da su kai ziyara a Afrika ta kudu.

An kafa hukumar gabatar da alamar Afrika ta kudu a shekarar 2002 da zummar yada da kuma kafa alamar Afrika ta kudu mai kyau. Wannan hukuma ta kafa ofishinta a nan birnin Beijing a shekarar bara, da nufin baiwa Sinawa wani dandali mai kyau wajen fahimtar Afrika ta kudu, ta yadda jama'ar kasashen biyu za su kara mu'ammala tsakanin su. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China