in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Afrika ta kudu zai kawo ziyara nan kasar Sin
2013-10-21 20:29:10 cri
Kakkakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, madam Hua Chunying ta bayyana a yau Litinin a nan birnin Beijing cewa, bisa gayyatar da takwaransa na kasar Sin, mista Li Yuanchao ya yi masa, mataimakin shugaban kasar Afrika ta kudu, mista Kgalema Motlanthe zai kawo ziyarar aiki nan kasar Sin daga ranar 27 zuwa 30 ga wata, inda shugabannin biyu za su shugabanci cikakken zaman taro karo na biyar na kwamitin kasashen biyu.

Madam Hua ta yi bayanin cewa, bisa tsarin kwamitin sassan biyu za su yi musayar ra'ayoyi sosai kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da batutuwan kasa da kasa da na shiyya-shiyya dake jawo hankulansu duka. Sin ta yi imanin cewa, ziyarar za ta inganta dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare dake tsakanin kasashen biyu a dukkan fannoni. Hua ta kuma bayyana cewa, Sin da kasar Afrika ta kudu manyan kasashe ne masu tasowa, kuma muhimman kasashen da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa, saboda haka, Sin na fatan yin kokari tare da Afrika ta kudu, don daga matsayin dangantakarsu zuwa wani sabon matsayi. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China