in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa da AU na fatan tsara wani shiri na tinkarar matsalar bakin haure
2015-10-06 14:25:27 cri
A jiya ne shugaban kasar Faransa François Hollande ya gana da shugabar hukumar zartarwar kungiyar AU Madam Dlamini Zuma wadda ke ziyarar aiki a kasar. Inda bangarorin biyu suka bayyana fatansu na bullo da wani daftari a taron koli na shugabannin kasashen Afrika da Turai da za a yi a watan Disamba na bana a kasar Malta, ta yadda za a warware matsalar bakin haure.

Madam Zuma ta yi kira da a ba da muhimmanci kan yadda za a warware wasu matsalolin da kasashen Afrika ke fuskanta, a cewarta, ana matukar bukatar bunkasa sha'anin noma na zamani don kawar da talauci, lamarin dake bukatar horas da matasa yadda ya kamata, da hana matasa ficewa daga kasashensu dalilin rashin aiki yi. Idan mutane suka mai da hankali kawai kan batun tsaro, zai matuka wahala a iya warware matsalar bakin haure, saboda babu wani matakin da zai dakatar dasu ba.

Bisa labarin da kafar yada labaru ta kasar Faransa ta bayar, an ce, hukumar EU ta ba da shawara a watan Satumba na bana a ganin an gaggauta kafa wani asusu na Euro biliyan 1.8 don tinkarar wannan matsala. Kuma taron shugabannin kasashen Turai da na Afrika da za a yi a watan Disamba a Valetta na kasar Malta, zai mai da hankali kan wannan matsala ta hanyar yin hadin gwiwa tsakanin kasashen da abin ya shafa. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China