in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi zanga-zanga a birnin Paris don nuna kin ta'addanci
2015-01-12 10:51:40 cri

An yi zanga-zanga a ranar 11 ga wata da yamma a birnin Paris dake kasar Faransa, inda manyan jami'an kasar, shugabannin kasashen duniya fiye da 40 da wasu shugabannin hukumomin duniya da na yankuna suka halarci jerin gwanon, ciki har da shugabar gwamnatin kasar Jamus Angela Merkel, firaminsitan kasar Ingila David Cameron‎, firaministan kasa Italiya Matteo Renzi, firaministan kasar Spaniya Mariano Rajoy, firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu, shugaban kwamitin kungiyar EU Jean-Claude Juncker da sauransu.

A wannan rana da karfe 3 da minti 25 da yamma, wadannan jami'ai daga kasa da kasa da shugaban kasar Faransa François Hollande sun yi jerin gwano tare da jama'ar kasar Faransa don nuna kiyayya ga ayyukan ta'addanci. Hakazalika kuma, an yi zanga-zanga a sauran birane da yankunan kasar a wannan rana. Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Faransa suka bayar, an ce, yawan mutanen da suka yi zanga-zanga a wannan rana ya kai fiye da miliyan daya.

Ministan harkokin cikin gida na kasar Faransa Bernard Cazeneuve ya bayyana a ranar 10 ga wata cewa, an yi zanga-zangar don nuna girmamawa ga mutanen 17 da suka mutu a kasar a sakamakon harin da 'yan ta'adda suka kai gare su a kwanakin baya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China