in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba a kawo karshen barazana a kasar Faransa ba
2015-01-10 17:39:17 cri

Shugaban kasar Faransa François Hollande, ya ce kasar sa na ci gaba da fuskantar barazana, don haka ya zama wajibi a maida hankali wajen dakile duk wani yunkuri na kaiwa kasar hari.

Jawabin na shugaba Hollande na zuwa ne jim kadan bayan da 'yan sandan kasar suka shawo kan wasu al'amura biyu masu alaka da yin garkuwa da mutane a kasar.

François Hollande wanda ya gabatar da wani gajeren jawabi a fadar sa, ya ce za a ci gaba da kaiwa kasar hare-hare. Don haka baya ga yabawa 'yan sanda game da matakan tsaro da suke dauka, ya kuma ya yi kira ga jama'ar kasar da su yi taka tsantsan, tare da hada kan juna. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China