in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faraministan Faransa ya yi kiran 'yan kasarsa da su fito kwansu da kwalkwata domin nuna jimaminsu
2015-01-11 17:00:22 cri
Bayan kawo karshen dauki ba dadi da murkushe masu hannu kan hare haren ta'addanci da yin garkuwa da mutane a birnin Paris a ranakun Laraba da Jumma'a, faraministan kasar Faransa ya yi kiran 'yan kasar Faranasa a ranar Asabar da su fito kwansu da kwalkwata a babban jerin gwanon na ranar yau Lahadi sha daya ga watan Janairu domin nuna jimaminsu ga mutanen da hare haren suka shafa.

'Yan ta'adda sun kai hari kan muhimman abubuwan kasar Faransa, wato 'yancin fadin albarkacin baki, da yin zane zane. An bukaci kawar da mujallar Charlie Hebdo, don haka ya kamata ta ci gaba da fitowa, in ji Manuel Valls a lokacin da yake gabatar da sakonsa na fatan alheri a Evry, da aka watsa ta kafofin kasar.

Jerin gwanon masu kishin kasa na ranar Lahadi zai kasance wani babban taron gangami na jama'a da zai kasance cikin tarihin kasar, tare da fatan jerin gwanon za'a yi shi cikin karfi, da sanin ya kamata da kuma nuna karfin kasa, da darajar al'ummar Faransa, dake bayyana soyayyarta da babbar murya ga 'yancinta da hakuri da juna. Ku zo da dama, in ji faraministan kasar Faransa tare da yin alkawarin tabbatar da tsaro.

"Ta'addanci na son ya raba mu, ya kawo baraka tsakaninmu, yana fatan tsoratar da mu domin mu tsaya cikin gidajenmu. Amsa mai kyau, shi ne 'yan kasar Faransa tun daga ranar Laraba sun ci gaba da fitowa nuna yin allawadai a ko ina cikin biranen kasa", in ji mista Valls. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China